Daga Yahaya M Abdullahi
A ranar Asabar ne hadaddiyar Kungiyar Matasan Afirka ta zaman lafiya wato ‘African Youth Assembly for Peace’ sun gudanar da gagarumin taro domin yaki da mummunan dabi’ar fyade a babban dakin taron Jami’ar Keffi dake jihar Nasarawa.
Taron wanda kungiyar Matasan suka shirya ya samu mahalarta da daman gaske daga sassa daban-daban na jihar Nasarawa. Babbar bakuwa a muhallin taron ita ce Uwargidan gwamnan jihar Nasarawa wato Hajiya Slififat A.A Sule mai kungiyar ‘SAS foundation’ sai dai ba ta samu damar halartar taron ba inda ta turo da wakiliyarta a muhallin.
Hajiya Habiba Sulaiman ta gabatar da jawabinta tare da jinjina ga wadannan matasan da suka shirya wannan taro, tare da kuma ba su karfin gwuiwa kan wannan yakin da suke yi da mummunan dabi’ar fyade.
Shima a nasa jawabin wanda ya wakilci mai girma Sarkin Keffin Magaji a muhallin taron, Abdu Usman Wamban Keffi ya jinjina ma taron tare kuma da yaba ma matasan a madadin Sarkin Keffi, inda ya roki matasan da ka da su canza akan abin da suke yi, su ci gaba da yaki da wannan mummunan dabi’ar fyade a jihar Nasarawa dama kasa baki daya.
An kammala taron lafiya, masana da daman gaske ne suka halarci taron tare da sa albarka da kuma takaitaccen jawabi akan mummunan dabi’ar fyade a muhallin. Cikin wadanda suka samu halartar taron harda Hajiya Zainab Muhammad, Kwanturola a hukumar lura da shige da fice ta Nijeriya (Immigration Service) da kuma Manyan Malaman Malaman Jami’ar.