JARIDAR DIMOKURADIYYA: Majalisar wakilan tarayyar Najeriya ta baiwa Shugaba Muhammadu Buhari sa’o’i 48 don yi wa ‘yan Najeriya bayani game da shirin Gwamnati da ta ke yi wajen dakile kisan gillar jama’a da ake yi da hukunta wadanda aka kama da laifi a kasar.
`Yan majalisar sun bukaci fadar shugaban kasa, Ministan tsaro, hafsoshin tsaro da Sufeta Janar na ‘yan sandan Najeriya da dai sauran masu fada aji, akan bullo da hanyar magance yawan kisan- gillar da ‘yan bindiga da barayi ke yi a kasar ke yi tare da hukunta su.