A jiya Alhamis Mutane Miliyan Dari tara ne A ke sa ran sun fara Kada Kuri’ar su domin zaben ‘Yan Majalisar Dokokin Kasar India, wacce ita ce Kasa ta biyu da ta fi yawan al’uma a duniya, inda ra’ayoyi tsakanin masu son Firaminista Narendra Modi, da kuma ‘Yan adawa da shi.
Zaben na wannan lokacin, Indiyawa miliyan 900 ne aka yi wa rajistar zaben wakilan majalisar dokokin su 543, a zaben da aka fara 11 ga watan Afrilu a mataki na farko.
Za kuma a kammala shi ne a ranar 19 ga watan gobe, sannan a kidaya kuri’u a ranar 23 ga watan na gobe.
Sama da mutane miliyan 84 ne da suka hada da matasan da ke zabensu na farko su miliyan 15 ke zabe a kashi na farko da ake yi a wannan Alhamis.
An dai zabi Firaminista Narendra Modi ne shekaru biyar da suka gabata tare da alkawuran kyautata tattalin arziki cikin gaggawa da kuma rage matasa marasa ayyukan yi.
Akwai dai ci gaba ta fannin hanyoyin mota da kuma na jiragen kasa cikin tsukin da ya yi a mulki, sannan mazauna yankunan karkara na yaba wa kokarin da ya yi wajen sama masu iskar gas na girki da a baya babu ita.
Jam’iyyarsa BJP na amfani da rikicin nan da ke tsakanin kasar da Pakistan, wajen janyo hankalin jama’a don ta sami kuri’u a zaben da ke Gabata.
To sai dai tattalin arzikin kasar ya ja baya kamar yadda bangaren samar da ayyukan yi shi ma ya fuskanci koma bayan da ba a ga irinsa ba sama da shekaru 45 da suka gabata.