Shirin bayar da gudunmawar fansho na jihar Jigawa da na kananan hukumomi ya ce ma’aikatan gwamnati 100 ne suka mutu a cikin wata guda.
Sakataren zartarwa na hukumar Alhaji Kamilu Aliyu Musa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai game da biyan kudaden fansho da na wadanda suka mutuwa a ofishin sa.
Ya ce hukumar ta biya Naira Billiyan 1.215 ga ma’aikata 550 da suka yi ritaya a watan Yulin shekarar 2022.
Kamilu ya bayyana cewa, wadanda suka amfana an kasasu kashi hudu domin biyansu hakkokinsu.
A cewarsa “Kashi na farko ya hada da mutane 411 da suka ci gajiyar aikin bayan sun yi ritaya daga aikin kuma an biya su sama da Naira miliyan 920,331.
“Kashi na biyu na wadanda suka ci gajiyar tallafin su ne iyalan mutane 100 da suka mutu yayin da suke hidimawa jihar, inda suka karbi adadin Naira miliyan 267,329.”
“Kashi na uku na masu cin gajiyar sun kai mutum 8 suna karkashin ma’aunin fansho na mutuwa kuma za su sami Naira miliyan 27, 952 a matsayin hakkinsu.”
“Yayin da kashi na hudu na wadanda suka ci gajiyar tallafin su ne wadanda ba su yi aiki ba har zuwa shekaru biyar, hukumar za ta mayar musu da kashi 8 bisa dari wanda ya kai Naira dubu 201,437 a matsayin hakkinsu.”
Sakataren zartaswar ya kuma jaddada alkawarin hukumar na biyan kowane ma’aikacin gwamnati da ya yi ritaya hakkokinsa a cikin wata daya da ya yi ritaya.
Kazalika ya yabawa Gwamna Muhammad Badaru Abubukar na jihar bisa goyon bayan da yake baiwa hukumar tare da sakin hakkokin ‘yan fansho a lokacin da ya dace.
A wani labarin kuma na daban.
Yanzu-Yanzu: Babu jarrabawa a ranar Sallah —NECO
Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta kasa (NECO) ta musanta cewa ta sake sanya ranar jarrabawar kammala sakandare ta SSCE da ta shirya yi a ranar Asabar 9 ga watan Yuli.
Ta bayyana cewa, maimakon haka, ta ba da cikakken mako guda ga daliban fomin hutu, daga ranar Juma’a 8 ga Yuli zuwa Laraba, 13 ga Yuli, 2022, don ba wa Musulmai adamar samun isasshen lokacin bikin na Sallah.
Wannan, a cewar shugaban sashen yada labarai da hulda da jama’a na NECO, Mista Azeez Sani a wata sanarwa da ya fitar a Minna, ya sabawa rade-radin da wasu ke yi na cewa hukumar ta tsara jarabawa a ranar 9 ga Yuli, 2022, wato ranar Sallah (Eid-Adha).
Sanarwar ta kara da cewa, “Hukumar NECO na so ta bayyana cewa ba ta sanya ranar yin jarrabawar ba a ranar Asabar 9 ga watan Yuli, 2022. Ta bayar da cikakken mako daya domin hutu ga zasu zauna jarabawar,, wanda ya fara daga ranar Juma’a 8 ga watan Yuli zuwa Laraba 13 ga Yuli, 2022 don baiwa Musulmai damar samun isasshen lokacin bikin.
“Tun da an san mahimmancin bukukuwan addini, hukumar ta NECO ta kan samar da isassun tanadin irin wannan wajen kayyade ranakun jarrabawa”.
Idan Za a iya tunawa cewa jarrabawar shaidar kammala sakandare ta 2022 (SSCE) ga masu rubuta jarabawar, an fara ne a ranar 27 ga Yuni, kuma ana saran kammalawa a ranar 12 ga Agusta, 2022.