By Abbas Yakubu Yaura
Kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa reshen jihar Legas a ranar Juma’a tace za ta fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku daga ranar Litinin mai zuwa.
Sakataren kungiyar na jihar, Oloruntoba Odumosu, a wata sanarwa daya fitar, yace yajin aikin ya zama dole domin tilastawa gwamnatin jihar Legas daukar matakin gaggawa kan bukatun su.
“Majalisar zartaswar kungiyar ta jiha a taronta na ranar 29 ga watan Disamba, 2021 ta yanke shawarar cewa majalisar zata fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku daga karfe 08:00 na safe a ranar Litinin, 10 ga watan Janairu, 2022 zuwa 08:00 na dare ranar Laraba, 12 ga watan Janairu 2022.
“Wannan yajin aikin gargadin shi ne don tilastawa gwamnatin jihar Legas daukar matakin gaggawa kan batutuwa kamar haka; matsanancin karancin ma’aikatan jinya da ungozoma a wuraren kiwon lafiya; biyan kuɗin riƙewa; ingantaccen tsarin albashi na CONHESS; daidaita ma’aikatan jinya da suka kammala karatun digiri da ma’aikatan aikin jinya; ingantattun jin daɗi da yanayin aiki na ma’aikatan jinya; ingantaccen izinin haɗari; wakilcin ma’aikatan jinya a cikin kwamitocin da suka dace da tsare-tsare inshorar rai ga ma’aikatan jinya da sauran ma’aikatan lafiya,” sanarwar ta kara da cewa.
Odumosu ya kara da cewa yajin aikin zai kasance baki daya tare da kebe cibiyoyin kiwon lafiya na tarayya a jihar.