• lamarin ya afaru ne a jihar kwara.
• Wata uwa ce ta Sha Maganin Gargajiyaa tare da iyalanta suka mutu har lahira.
• Kwamishinan yan sandan jihar ya tabbatar da afkuwar lamarin inda kuma ya ja hankalin al’umar jihar, da su kaucewa afkuwar hakan a gaba.
Mutun 10 da suka fito daga ahali daya na kabilar Fulani sun mutu a jihar Kwara, biyo bayan sun sha wani maganin gargajiya da a kace maganin ciwon kafa ne.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar Kwara, SP Ajayi Okasanmi, ya tabbatar da faruwar lamarin ta cikin wata sanarwa da ya fitar a yau laraba a garin Ilorin babban birnin jihar.
A cewar sa, a ranar Talata 22 ga watan nan ne da misalin karfe bakwai na safe, wani Ba-fulatani mai suna Ibrahim Bonnie, ya kawo rahotan faruwan lamarin zuwa ga ofishin yan sanda da ke yankin Gwanara.
A cewar sa, “Wani mai suna Okosi Musa da Worugura Junlin ne su ka zo wurin Mahaifiyar shi, mai suna Pennia Bonnie, da su ke zaune tare da ita a sansanin guda , kuma take fama da ciwon kafa, su ka bata wani maganin gargajiya da suka ce, shine maganin cutar dake damun ta, inji shi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kuduri mai mahimmanci da Sanata Uba Sani ya gabatar a Majalissar dattijai
Inda wadanda a ke zargin su ka cewa matar, da ta tabbatar dukkannin iyalanta sun sha maganin gargajiya, domin tabbatar da kauce wa yaduwar cutar ga sauran iyalan na ta, inji shi
“Sai dai jim kadan bayan sun sha maganin ne suka fara mutuwa daya bayan daya, inda a nan ne mutun koma suka mutu harda mahaifiyar ta shi” a cewar sa
Inda ya Kara da cewa kwamishinan yan sandan jihar, ya shawar ci al’umar da su dunga ziyartan kwararru a fannin kiwon lafiya, domin kauce wa afkuwar hakan a gaba.
A karshe ya ce, Dazaran an kammala gudanar da bincike za a gurfanar da wadan da ake zargi a gaban kotu” inji shi
Comments 1