By Abbas Yakubu Yaura
An tsige mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Imo, Amara Iwuanyanwu.
An tsige shi ne yayin zaman majalisar a ranar Talata.Kafin tsige shi, Ekene Nnodim, mai wakiltar mazabar jihar Orlu, ya gabatar da kudiri mai dauke da sa hannun ‘yan majalisa 18 daga cikin 27.
Kakakin majalisar, Paul Emezim, wanda ya jagoranci zaman majalisar, daga bisani ya amince da tsige Iwuanyanwu.
Majalisar ta kuma kirayi ‘yan majalisar dokokin jihar guda shida da aka dakatar.Hakan dai ya zo ne watanni hudu bayan Emezim ya dakatar da ‘yan majalisar bisa zargin rashin da’ar majalisa.
Sai dai Dakatarwar ‘yan majalissun ta janyo suka daga al’ummar jihar.Amma a ranar 6 ga watan Oktoba wata kotu a Owerri ta soke karar dake kalubalantar dakatar da ‘yan majalisar guda shida.
Lauyan ‘yan majalisar da aka samu rikici, Kingdom Okere, yace an kai karar ne bayan abokan huldar sa da shugabannin majalisar sun cimma matsaya.
A ranar Talata ne shugaban majalisar ya sanar da cewa ‘yan majalisar da aka dakatar sun tuba a saboda haka an dage haramcin watanni hudu da aka kakaba musu.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa ‘Yan majalisar dai sun hada da Kennedy Ibe, Onyemaechi Njoku, Uche Ogbuagu, Anyadike Nwosu, Philip Ejiogu da Dominic Ezerioha.