By Abbas Yakubu Yaura
Majalisar dokokin Najeriya ta bayyana goyon bayanta ga shirin rigakafin cutar COVID-19 na wajibi ga ma’aikatan gwamnatin tarayya da na jihohi.
Shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin kiwon lafiya a matakin farko da cututtuka masu yaduwa, Chukwuka Utazi, shine wanda ya shaida wa wakilinmu a wata tattaunawa da ya yi da shi ranar Talata a Abuja, kan cewa dokar tana da cikakken goyon bayan majalisar tarayya.
Sannan ya ce majalisar dokokin kasar nan za ta yi duk mai yiwuwa don ganin cewa babu wani dan Najeriya da ya ki amincewa da allurar.
Ya Kara da cewa “Majalisar ba ta bambanta da na zartarwa ba domin ita gwamnatin tarayya daya ce. Dukanmu mun damu da lafiyar mutane da yadda za a kare mutuwar da ba a so.
Sanatan ya ce duk wanda ya ci gaba da shiga harabar gwamnati dole ne a yi masa alluran rigakafi don kada a sanya rayuwar wasu a cikin mawuyacin hali.
“Muna so mu yi wa mutane alluran rigakafi domin mu kare al’ummarmu. Idan aka duba kaso na wadanda aka yi wa allurar, kuma aka kwatanta da sama da mutane miliyan 200, ba shi da wani muhimmanci ga rigakafin.” Idan aka kwatanta da sauran yanayi, kaso na wadanda aka yi wa allurar, adadin ya yi kadan a Najeriya. “