By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin tarayya ta tabbatar wa ‘yan majalisar wakilai kudirin ta na tabbatar da samar da isassun kudade na manyan tituna masu karfin tattalin arziki a fadin Najeriya.
Babban sakatare na ma’aikatar ayyuka da gidaje ta tarayya Hassan Musa ne ya bada wannan tabbacin a ranar Talata a Abuja, yayin da yake jawabi ga ‘yan majalisar daga jihar Borno da suka hada da shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, Muktar Betara; Ahmadu Usman Jaha, da Kabir Tukura, wadanda suka ziyarci ma’aikatar.
Musa ya ce ma’aikatar ta samu sabbin kudade na hanyar tarayya daga Gombe zuwa Biu, inda ya tabbatar wa ‘yan majalisar cewa majalisar zartarwa ta tarayya za ta amince da aikin gyaran da sauran zababbun hanyoyin gwamnatin tarayya a fadin kasar nan.
Sannan ya ce, “A madadin gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma mai girma minista, Babatunde Raji Fashola, ina so na tabbatar da cewa muna samar da sabbin kudade don gudanar da wannan aikin hanyar kuma za a ba dan kwangilar duk wani abin da ya dace domin ya samu damar gudanar da ayyukan hanyar.
Betara wanda ya jagoranci tawagar ya jaddada bukatar samar da wasu kudade na daban domin aikin hanyar Gombe zuwa Biu. Ya bayyana damuwarsa kan halin da hanyar ke ciki duk da kasafin da ake ware wa aikin duk shekara. Sai dai ya lura cewa kudaden ba su isa ba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “An bayar da kwangilar hanyar Gombe zuwa Biu shekaru biyar zuwa shida da suka gabata kuma dan kwangilar yana tafiyar hawainiya sosai. A duk lokacin da muka tattauna da shi, matsalarsa ita ce kudade, domin ba za a iya samun kudaden gudanar da irin wannan aiki ta hanyar kasafin kudi ba.
“Duk da cewa ni ne shugaban kwamitin kasafin kudi, amma ina da iyaka kan yadda zan iya sanya hanya a mazaba ta. Don haka, na yanke shawarar zuwa in ga Babban Sakatare da Mai Girma Minista don yin roko.Kuma ina farin ciki a yau;ya sanar da ni cewa akwai taga don tallafawa aikin hanyar Gombe zuwa Biu a kasa.
Comments 1