By Abbas Yakubu Yaura
Akalla mutane 18 ne suka mutu bayan da wata mahakar zinari ta rufta a kudancin Nijar kusa da kan iyaka da Najeriya, kamar yadda magajin garin yankin ya bayyana a ranar Litinin.
Magajin garin Dan-Issa, Adamou Gueraou, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, “Mutane 18 ne suka mutu na wucin gadi, wadanda muka binne su da safiyar yau.”
“Haka zalika akwai bakwai dake kwance a asibiti da suka samu raunuka,” in ji shi, ya kara da cewa ‘yan Najeriya na cikin wadanda hatsarin ya rutsa dasu kuma sun jikkata.Ya kara da cewa, hatsarin ya afku ne a lokacin da rijiyoyin sana’o’in hannu suka rufta a mahakar ma’adinan Garin-Liman da yammacin ranar Lahadi.
“Har yanzu ana ci gaba da ayyukan ceto, ana iya samun gawarwakin da suka makale a kasan ramuka,” in ji wata majiya a yankin.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa An gano mahakar ma’adinan Garin-Liman ne ‘yan watannin da suka gabata, amma dubban masu hakar ma’adanai ne suke yin tururuwa zuwa yankin dan neman abin sanyawa a bakin salati.
Shekaru da dama, ma’adinan zinare na Nijar na jan hankalin masu kallo, musamman a yammacin yankin Tillaberi, inda a yanzu ke fama da munanan hare-haren ‘yan jihadi, da kuma arewacin kasar dake kusa da iyakar Libya.
Hatsari a wadannan wuraren na yawan faruwa ne saboda rashin kwanciyar hankali da kuma tsofaffin hanyoyin da masu hakar ma’adinai ke amfani dasu, a cewar hukumomi.
An rufe ma’adinan zinare da yawa a cikin shekarar 2017 a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnati na sabunta masana’antar.Tun daga shekarar 2004, Nijar na da ma’adinan masana’antu guda daya a Samira dake yankin Tillaberi.