-Zai Kafa Dokar ta baci kan ilimi, ya bukaci sarakuna su tsuke bakinsu kan siyasa.
Dazu da rana sabon Gwamnan ya fadi haka a yayin bikin rantsar da shi a garin Gusau.
Matawallen na Maradun, wanda ya nunawa masu kai hare hare da Garkuwa da mutane a jihar yatsa. Yana mai. Shawartarsu da su tuba, ko kuma su yi hanzarin barin jihar.
Daga nan ya ja kunnen ‘yan-sa-kai masu rafke wadanda aka kama da zargin kai hari ko satar jama’a, ba tare da gurfanar da su a kotu ba su daina, don gwamnatinsa ba za ta lamunci haka ba.
Matawalle ya kuma ce zai kafa dokar ta baci kan ilimi, ta yadda dukkanin ‘ya’yan jihar ya zama wajibi su je makaranta.
Gwamna Matawallen Maradun, ya gargadi sarakuna da su kiyayi kan su da shiga harkokin siyasa.