Matasan jam’iyyar APC sun roƙi tsohon mataimakin Shugaban ƙasa kuma tsohon ɗan takarar shugabancin ƙasar nan Alhaji Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki da su sake dawowa jam’iyyar.
Gamayyar ƙungiyar matasan ta buƙaci Atiku da Saraki da kuma tsohon gwamann Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Gwamna Aminu Tambuwal na Sakkwato da Sanata Dino Melaye da sauran ƙusoshinta da suka sauya sheka da su dawo kafin zaɓen 2023.
“Muna maraba da dukkan tsoffin ‘yan jam’iyya da suka sauya sheƙa su duba yiwuwar dawowarsu, domin APC ta gaskiya za ta sake bayyana a babban taron da ke tafe, domin ci gaba da kyawawan ayyukan da ta faro a Najeriya”, inji su.
Shugaban ƙungiyar matasan Iliyasu Ibrahim Makinta ya yi kiran ne a Kaduna a lokacin wani taron manema labarai da suka gudanar a ranar Alhamis.
Makinta ya yaba da yadda shugaban riƙon APC, Gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe da ‘yan kwamitinsa ke ƙoƙarin ɗinke ɓarakar da ke cikin jama’iyyar.
https://dimokuradiyya.com.ng/tinubu-ya-nemi-atiku-ya-dawo-apc/
Ya ce yadda Buni ya shawo kan tsohon Shugaban Majalisar Wakilai, Yakubu Dogara ya dawo jam’iyyar bayan ya bar ta abun sha’awa ne.
“Muna roƙon gwamnoni da dukkannin ‘yan jam’iyya da su tsagaita rikicin domin an ga shaida cewa kwamitin Buni na ƙoƙarin damawa da kowa.
Mutanen da ake roƙon sun fice daga APC ne bayan rikicin cikin gida da ya kunno kai a jam’iyyar gabanin zaben 2019.
A baya jam’iyyar APC ta yi musu irin wannan kira, bayan dawowar Dogara da da Sanata Barnabas Gemade daga Jihar Benuwe.
Sai dai Saraki da Atiku sun yi watsi da tayin, ta bakin masu magana da yawunsu, wanda suka ce komawa APC kasada ce, domin jam’iyyar na gab da rushewa.