Wakilinmu Uzairu Sulaiman
Biyo bayan takaddamar dake faruwa a jahar Kano sakamakon takardar tuhuma da Gammatin jahar ta aikewa sarki Sanusi na biyu bisa zargin badakala da baitulmalin Masarautar Kano, Ya sanya hukumar karbar korafe korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jahar Kano fitar da matsaya kan batun.
Takardar da aka rabawa manema Labarai dauke da sa hannun Shugaban hukumar Muhuyi Magaji Rimin Gado ta bayyana cewa batun binciken cin hanci a baitulmalin Masarautar Kano ba ya fara ne a lokacin sake hawan wannan gwamnati ta Gwamna Abdullahi Ganduje bane.
“Hukumar ta karbi korafi daga abokan Masarautar Kano a ranar 28 ga watan Maris, 2017 kan zargin sarkin Kano Sanusi na biyu da badakala da kudin Masarautar Ta Kano. Korafin yayi nuni da zargin kashe kudaden Masarautar ba ta sahihiyar hanya ba” a cewar takardar.
Takardar ta Kara da cewa karbar korafin ke da wuya kasancewarta mai cin gashin kanta, ta fara gudanar da bincike karkashin tanadin dokar hukumar ta jahar Kano, doka ta 8, da 9, da ta 15 ta shekarar 2008 da aka yiwa kwaskwarima.
Takardar ta Kara da cewa tazo gabar da doka ta bata damar aikewa gwamnati lamarin dake faruwa ne don hukumar ta samu damar cigaba da bincike ba tare da samun wani tsaiko ba.
Sai ta kara da cewa sanya bakin mahukunta cikin lamarin shi zai bawa hukumar sakin mara don cigaba da binciken karar dake gabanta kan masuratar ta Kano, sakamakon cikas da binciken ke cin karo dashi a Masarautar.
Takardar daga nan sai tayi Kira ga jama”a kan su sani cewa an fara gudanar da binciken ne a Masarautar tun a shekara ta 2017 ba 2019 ba.
Sanarwar ta kara da cewa, hukumar karbar korafe korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jahar Kano bata karkashin wani ko wasu mahukunta da zasuyi karan tsaye ko son zuciya ga tsare tsaren hukumar.
Sai tace “rahotonmu na farko shine Kawai yana bukatar gwamnati ta dauki matakan tsarin gudanar da mulki Wanda zai bawa hukumar damar cigaba da bincikenta ba tare da katsalandan ba. Don haka binciken mu nakan gudana a halin da ake ciki “.
Daga bisani takaradar tayi fatan za a sakarwa lamarin yaki da cin hanci da rashawa mara a Najeriya domin tsarin ya cimma nasara.