Jam’iyyar PDP a jihar Kwara ta zargi Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da hada hannu da wani kamfani da Hukumar Kula da Al’amuran harkokin kasuwanci (CAC) ta ayyana a kwance a asusun jihar.
A makon da ya gabata ne gwamnan ya ce an wawure sama da Naira biliyan 11.9 na kudaden jama’a a baitul mali tsakanin shekarar 2011 zuwa 2019 inda ya ambato wani binciken kwakwaf da SSAC Advisory and Professional Limited ya yi.
KARANTA WANNAN LABARIN: An Kama Direban Motar Dangote Kan Laifin Yin Jigilar Kaya Ba Bisa Ka’ida Ba
Amma jam’iyyar adawa a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta, Prince’Tunji Moronfoye, ya fitar, ta kalubalanci gwamnan da ya “buga ta yanar gizo da kuma kan layi da takardun kwangila da kudaden da aka biya na ayyukan.”
Ta ce sakamakon binciken da hukumar ta CAC ta fitar ya nuna cewa kamfanin binciken kudi da gwamnatin jihar ta dauka ba ya aiki.
“Yana da kyau a tunatar da Kwara cewa mai binciken waje ba shi da hurumin duba asusun jihar. Irin wannan iko ya rataya ne ga babban mai binciken kudi na jihar Kwara wanda doka ta ba shi ikon gudanar da bincike,” inji sanarwar.
Sai dai da yake zantawa da Daily Trust a jiya, mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin sadarwa, Alhaji Bashiru Adigun, ya ce jam’iyyar PDP ta jajirce ne kawai, inda ya shawarci duk wanda ke da hannu a zamba da su dawo da abin da aka sace kafin lokaci ya kure musu.
“Su (PDP) ba su da gaskiya a kansu. Ba a janye takardar shaidar kamfanin ba kuma har yanzu kamfanin yana da rajista da Hukumar Kula da Harkokin Kasuwanci (CAC).”
“Idan suna da wata matsala da kamfanin, to su kai su kara. Shin matsayinsu na PDP ya bata sakamakon binciken da hukumar binciken ta yi?”
“Duk da haka, an mika sakamakon binciken hukumar binciken ga ma’aikatar shari’a kuma suna duba ta don ganin abin da za su iya yi a kai. Duk wanda ake tuhuma zai samu ranar a kotu,” Adigun ya kara da cewa.
A wani labarin kuma, Tintuni Tinubu Da Arzikinsa Tun Kafin Ya Shiga Siyasa — Dele Alake
Daraktan yada labarai da dabarun yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Dele Alake ya kare tushen arzikin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Asiwaju Bola Tinubu, inda ya ce ya san Tinubu yana da arziki tun kafin ya shiga harkokin siyasa.
Alake, wanda ya yi wannan ikirari a wata hira da gidan talabijin na Channels Sunday Politics, ya lura cewa Tinubu ya yi kasuwancinsa da ciniki kuma yana da hannun jari tsawon shekaru don gina dukiyarsa.