A yayin da Nijeriya ke cika shekara 59 da samun ‘yancin kai, hukumar ba da agajin gaggawa ta kasa wato NEMA sun karbi tawagar ‘yan Nijeriya 161 da suka dawo daga kasar Libya bayan an bar su yashe a kasar ta Libya.
Alhaji Idris Muhammed, Kodinaten hukumar NEMA din reshen Legas, shi ne ya tabbatar da hakan a ranar Talata a Legas.
Muhammed ya ce; ‘yan Nijeriyar sun iso filin jirgin Murtala Muhammed dake Legas ta Cargo da misalin karfe 5.35 na safiyar ranar Talata. Ya ce wadanda suka dawo sun dawo ne ta jirgin Al Buraq Air aircraft mai lamba 5A-DMG daga birnin Misrata City kilomita 200 zuwa babban birnin Tripoli na Libya.