Rikici mai kama da na kabilanci ya barke a garin Tigno Lamurde dake jihar Adamawa.
Ganau sun shaida mana cewa ‘yan Kabilar Batchama ne suka afkawa mutanen garin wadanda yake su kuma Hausawa ne. Majiyarmu ta tabbatarwa da Jaridar Dimokuradiyya cewa rikicin ya auku ne a yau din nan.
Har ya zuwa hada wannan rahoton da misalin karfe 2:40 na rana, babu wani dauki da jama’ar garin suka samu daga jami’an tsaro kamar yadda majiyarmu ta tabbatar mana.
Sannan hotuna da bidiyo da Jaridar Dimokuradiyya ta ci karo da su sun nuna yadda aka killace matan garin a wuri guda, a yayin da mazajensu kuma suka tunkari ‘yan kabilar Batchama din domin kare kawukansu da garinsu.
Duk wani kokari da majiyarmu ta yi na jin ta bakin mahukunta a jihar, abin ya ci tura.