Shugaban kasar Mali Ibrahim Bubacar Keita cikin daren ranar Asabar a jawabin da ya gabatar zuwa ‘yan kasar ya sanar da rushe majalisar fasalta kudin tsarin mulki.
Shugaban kasar ta Mali yayi Ibrahim Boubacar Keita ya na mai cewa a shirye yake don ya gana da sauren yan siyasa na kasar ta Mali, sanarwar dake zuwa yan lokuta bayan da Fira-ministan kasar Boubou Cisse, ya yi alkawarin gaggauta kafa sabuwar gwamnati da za ta tafi tare da ‘yan adawa, gami da kiyaye bukatun al’ummar kasar.
RFI Hausa ta labarto cewa; ‘yan Sanda na ci gaba da farautar wasu daga cikin jama’a biyo bayan zanga-zanga da ta rikide zuwa tarzoma a babban birnin kasar Bamako, abinda ya kai ga rasa rayukan akalla mutane 4, da jikkatar wasu sama da 20.