Rahotanni sun bayyana cewa, dakarun Brigade ta 21 masu sulke sun ceto wasu ‘yan matan makarantar Chibok biyu da aka sace a jihar Borno.
Zagazola Makama, kwararre a fannin yaki da tada kayar baya a yankin tafkin Chadi, ya bayyana cewa sojojin sun gano ‘yan matan biyu da aka bayyana sunayensu da Hannatu Musa da Kauna Luka a karamar hukumar Bama a ranar 26 ga watan Yuli, shekaru takwas bayan sace su a ranar 14 ga watan Afrilu shekarar 2014.
Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa ‘yan matan sun tsere ne daga sansanin Gazuwa, hedikwatar kungiyar Jama’atu Ahlus Sunna ta lid-Da’awah wa’l-Jihad ta Boko Haram, wadda ake kira Mantari da Mallum Gabchari, da ke da tazarar kusan kilomita 9 zuwa garin Bama.
Kubucewar ‘yan matan na iya rasa nasaba da ci gaba da kai hare-haren da sojojin Operation Hadin Kai suka yi wanda ya haifar da yunwa da kaura a yankunan ‘yan ta’addar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Tinubu Ta Gana Da Wasu Gwamnoni, Da Masu Ruwa Da Tsaki A Abuja
Rahotanni sun ce sojojin da ke garin Bama ne suka bayyana sunayen ‘yan matan biyu wadanda kuma za su tabbatar da lafiyarsu kafin su sake haduwa da iyalansu.
Idan ba a manta ba a makonnin da suka gabata sojojin sun ceto ‘yan matan Chibok biyu: Mary Dauda da Hauwa Joseph bayan sun tsere daga sansanin.
A wani labarin kuma na daban.
Abun Fashewa Ya Tarwatse, Ya Hallaka Tubabban Yan ta’adda 8 A Bama
Kimanin tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram guda takwas ne suka rasa rayukansu, daya kuma ya jikkata yayin da wani abun fashewa (IED), ya tarwatse a wani wurin zubar da shara da ke karamar hukumar Bama ta jihar Borno a ranar Litinin, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
An samu labarin cewa tsaffin ‘yan ta’addan na daga cikin mutane 800 da aka dawo da su garin Bama kwanan nan inda aka tsugunar da su a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke Bama.
Kafin faruwar lamarin Tubabbun ‘yan ta’addan da aka ce sun fito ne daga garin Bama da laifin yin mu’amala da wasu ’yan ta’addan na Boko Haram a wata kasuwa da ake kira “Daula” da ke wajen kauyen Goniri a garin Bama.
Zagazola Makama, wani kwararre a fannin yaki da yan tada kayar baya a tafkin Chadi, ya ce tsaffin ‘yan ta’addan sun karbi tarkacen daga hannun tsoffin abokan aikinsu (Boko Haram), wadanda har yanzu suke buya a dajin Sambisa ba tare da sanin cewa wasu daga cikin kayayyakin sun hada da wani bam da bai tashi ba. wanda aka yi watsi da shi bayan harin da sojoji suka kai.
Majiyar ta ci gaba da cewa, ciniki tsakanin tsoffin ‘yan Boko Haram da abokan aikinsu na baya ba wani sabon abu ba ne, inda ta ce a lokuta da dama idan suka ba su tarkace sai su rika musayar kayan abinci, kamar masara, gishiri, da Maggi da sauran su. -kayan masarufi kamar su tufafi, fetur da magunguna.
“Bayan sun karbi kayayyakin, za su zauna a bayan garin Bama don warwaresu su kafin su shigo da su cikin garin don sayar wa wakilansu. Suna cikin aikin warwarewar ne sai wani bam din ya tashi, inda nan take suka kashe takwas daga cikinsu yayin da daya daga cikinsu ya tsira da raunuka.