Rundunar ‘yan sanda reshen jihar Legas ta ce ta kama wani matashi Emeka Emmanuel dan shekara 29 a Ijaniki da ke unguwar Iyana Iba a yayin da ya ke yawo a gari yana nuna shi jami’in hukumar yaki da cin hanci da rashawa wato EFCC ne domin damfarar jama’a.
Rundunar ta bayyana hakan ne a wani sanarwa da ta fitar ta hannun Kakakinta, DSP Bala Elkana, a ranar Lahadi. Elkana ya shawarci al’ummar musamman masu neman aiki da su kula da ‘yan damfara a yyain da suke neman aikin domin kada su fada hannun wasu daga cikinsu.
A cikin sanarwaan ya ce, shi wanda ake zargin akan kama shi da shaidar zaman ma’aikacin hukumar EFCC ta bogi wanda ya ke amfani da shi yana damfarar mutane.
Wani bawan Allah, Olaposi Semiu da ke Agbara, ya shiga hannun shi wanda ake zargi inda shi wanda ake zargi (Emmanuel) ya karbi naira N51,000 a hannunsa a watan da ya gabata. Sanarwa ta kara da cewa, wannan kudin da bawan Allahn ya ba shi ya kasance kudin da zai yi amfani da shi wajen samar dan cikinsa aiki a hukumar EFCC.
An samu labarin cewa shi wanda ake zargi ya yadda da laifinsa, nan ba da jimawa za a mika shi ga kotu.