Har yanzu ba a fara gudanar da babban taron kasa da na fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki ba bayan sa’o’i uku.
Taron dai kamar yadda shirin ya nuna zai fara ne da misalin karfe 1:30 na rana a dandalin Eagle Square da ke Abuja inda gwamnonin APC da ‘yan majalisu suka iso.
Baya ga wakilan kasa daga wasu jihohi, jiga-jigan jam’iyyar da sauran masu ruwa da tsaki, har yanzu ba su isa wurin da karfe 4:30 na yamma ba.
Wakilai daga Kaduna, Imo, Jigawa Gombe, Borno, Enugu, Edo, Benue, Bauchi suma basu iso ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto da karfe 4:30 na yamma..
Gwamnonin jam’iyyar APC, shugabannin majalisar wakilai na jihar da na Tarayya wakilai, da masu neman takarar shugaban kasa, Yemi Osinbajo, da shugaban kasa Muhammadu Buhari, za su isa filin tsakanin karfe 1:30 na rana zuwa karfe 3:15 na rana, kamar yadda aka tsara abaya.
Sai dai daga Gwamna Atiku Bagudu, shugaban kungiyar gwamnonin na APC, da ‘yan majalisar dokokin kasa kadan, ne suka Isa wurin, yayin a wasu ba su iso ba.
An shirya cewa, za’a sa taken kasa don fara bude taron a hukumance da karfe 3:30 na rana. Sai dai har yanzu ba a fara gudanar da Taron ba da karfe 4:30 na yamma ba, lokacin da aka tsara cewa Gwamna Bagudu na jihar Kebbi, Kuma Shugaban gwamnonin jam’iyar APCn nakasa zai yi jawabi.
A wani labarin Kuma Makamancin wannan.
Da-Dumi-Dumi: ‘Yan takarar shugaban kasa 7 sun yi fatali da jerin sunayen yan takara 5 da gwamnonin APC suka mikawa Buhari
Wasu ’yan takarar shugaban kasa guda bakwai a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) sun yi watsi da sunayen mutane biyar da aka mikawa shugaban kasa Muhammadu Buhari , kamar yadda gwamnonin Arewa suka yi tun da safiyar yau
‘Yan takarar dai sun nuna rashin amincewarsu da cewa ba a tuntube su ba kafin gwamnonin Arewan su kai ga wannan matakin.
Wadanda ke neman takarar akwai gwamnan jihar Cross River, Ben Ayade; tsohon karamin ministan ilimi, Emeka Nwajiuba; tsohon ministan kimiyya da fasaha, Ogbonnaya Onu; tsohon Gwamna Rochas Okorocha da dan kasuwa Tein Jack-Rich.
Sun bayyana hakan ne a wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar ranar Talata, inda suka nesanta kansu daga cikin jerin sunayen da gwamnonin APC dake Arewacin suka fitar .
Sunayen da aka mika wa Buhari sun hada da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu; tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi; Gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi da mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo.