Jaridar The Nation ta rawaito cewa babban kotun tarayya da ke zama a Legas ya sa ranar 5 ga Watan Nuwamban a matsayin ranar da za a saurari karar da a ka kai Taurarauwar Mawakiyar nan Tiwa Savage.
Olumuyiwa Danladi wanda aka fi sani da Danny Young ne ya maka Mawakiya gaban alkalin babban kotu.
Danny Young na neman Alkali mai shari’a Mohammed Liman na babban kotun tarayyar yasa Tiwa Savage ta biya shi wasu kudi har Naira miliyan 205 kan amfani da basirarsa wajen rera wata waka da ta sanyawa suna ‘ONE’.
Danny Young ya ce an ci da guminsa ba tare da izininsa ba.
Mai tuhumar ya kuma maka kamfanin Marvin Records a wannan kara. Don Jazzy wanda ya yi fice a fadin Nahiyar Afrika shi ne ya kafa wannan kamfani shekaru bakwai da suka wuce.
Mawakin da ya yi tashe da wakarsa ‘Omo Lepa’ yana bukatar a biya shi fiye da Naira miliyan 200 ne da nufin ya rage zafi a kan satar basirarsa da aka yi wajen rera wata wakar da ya yi. Lauyan Mawakin ya kuma bukaci karin Naira miliyan biyar daga hannun Mawakiyar.
Har ila yau, wannan Mawaki ya nemi kotu ta ba shi duk ribar da aka samu daga wakar ta “ONE.” Justin Ige shine Lauyan mai kara a shari’ar da aka sa za a yi a Ranar 5 ga Wata.