Daga Mu’azza Yakubu Sanka
Shugaban Hukumar Sauraren Kararraki da Zargin Cin Hanci da Rashawa ta Kasa Reshen Jihar Kano, Wadda Barista Muhuyi Magaji, ke Jagoranta ta yi mana fashin baki dangane da mutane 29 da take Bincika kan badakalar kudi har sama da naira Miliyan Dubu Uku.
Wasu daga cikin Mutane 29 da Binkice ya zayyana sunansu sun zo sun amsa tambayoyin da mukai musu kuma sun tafi lafiya wasu kuma sun ki zuwa kuma sun koma bayan fage suna ta iface-iface bayan kuma muna da hujjoji birjik a kan su.
Cikin Wadanda muka gayyata har da matar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, da matan Sarkin Kano marigayi Ado Bayero a bisa gundarin Wasu tambayoyi da muke son su amsa mana.
Farko mun Gayyace su ne Bisa Sunayen su da muka ga sun gitta a wani kudi cikin kudaden da muke tuhumar masarauta da yin watandar su ba bisa ka’ida ba Wanda daga baya muka janye gayyatar muka Ce su rubuto mana amsar tambayoyin mu.
Dan haka ya kamata Ku ‘yan Jarida da sauran Al’umma mu gane cewa Gayyata Ce muka Janye amma Tuhuma na nan domin mu ba cewa muka yi wane mai laifi ba ne ko wance cewa muka yi zo ka amsa tuhumar da ake maka kan kaza da kaza shi kenan sai ka fara bam-bami su sauran da suka zo me ya same su.
Domin a bayanin da wadanda muka gayyata suka zayyana mana ya nuna cewa wani tsagi na wadannan kudade matar Marigayi Ado Bayero, da Matar sarki sunusi na II, sun karbi wasu kudade daga cikin kudin domin kula da lafiyar su ko mu ce sun sha magani da su.
Kazalika a baya Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito yadda hukumar ta zargi Sarkin Kano da yin Watandar Kudaden Masarautar da kashe kudi Ba Bisa Ka’ida ba Sannan kuma ta buga labarin yadda Sarkin ya Kare Kansa daga Tuhumar da cewa shi sam bai gaji Naira Miliyan Dubu Uku da Doriya ba Hasali ma Inji Martanin Naira Biliyan Daya da Miliyan Dari Takwas ya Gada.
Alhali yanzu haka muna da wani Asusu da muke kan Binkice da zaran mun gama za mu saki bayanin sa wanda muke ganin kudaden da muka ambata a baya na yanzu za su haura na da domin an yi amfani da wannan Asusun wajen Sutale Kudade Masu yawan gaske daga Fada, inji shi.
Amma abin da zai ba ka mamaki a nan shine sai masarautar ta nemi kotu ta dakatar da binciken. Wannan shine Karo na Biyu da Fadar Sarautar Sarki Sunusi na II ke neman kotu ta ba da umarnin a tsaida binciken da muke yi, na dauka tun da suna cewa Binkicen da muke yi ba Hujja a cikin sa wai Bita da Kulli ne Inji su, Ba Kamata yayi su bari mu gama ba?
Tun da ba laifi to ta Ina za mu kagoshi mu Ce an yi, amma kuma tun da yanzu duniya ta fahimci Masarauta na Ojiyo-Jiyo da Yunkurin kawo ma Binkicen mu Tasgaro me hakan ke nufi kenan? ai Ciki da Gaskiya Wuka ba za ta Huda ba.