A ranar Asabar ne rundunar ‘yan sanda ta jihar Ribas ta yi bajin kolin wani gawurtaccen da ya yi kaurin suna wajen kashe mutane mai suna Gracious David West. Inda ake zarginsa da hannu a kan kashe ‘yan mata a garin Fatakwal
Da ya ke yin bajin kolin na wanda a ke zargin, Kwamishinan ’yan sandan jihar, Mustapha Dandaura ya bayyana jindadinsa a kan nasarar cafke wanda a ke zargin da kuma yadda ake kara yawan samun karuwar kisan mutane a otel-otel dake cikin jihar da kuma matakan da rundunar ke dauka don magance hakan.
Kwamishinan ya kuma bayar da tabbacin ci gaba da gudanar da bincike a kan lamuran, inda ya ce, in an kammala za a maka wanda ake zargin a kotu.
Da yake yiwa ‘yan jarida bayanai Gracious David West ya bayyana cewa, an cafke shi ne a cikin wata motar bas a lokacin da ya yi kokarin guduwa zuwa jihar Akwa Ibom .
Gracious David West ya dai musanta aikata laifin da ake zarginsa da aikatawa, inda ya ce ya kashe mutum biyar a garin na Fatakwal ne kadai; daya kuma a yankin Owerri da kuma wani a jihar Legas.
Wanda a ke zargin Gracious David West ya fito ne daga karamar hukumar Asari-toru da ke cikin jihar ta Ribas ya kuma dantanta aikata ta’asar tasa ga aiki na shedan.
Kafin dai a cafke shi yana kai wandanda yake kashewa ne otel, don ya hallaka su ta hanyar shake su.
A dai cikin watanni goma da suka wuce, Gracious David West ya samu nasarar hallaka ‘yan mata goma da suka fada a cikin tarkonsa a garin Fatakwal da kuma daukacin fadin jihar ta Ribas.
Kisa na ranar Lahadin wancan makon da ya wuce, shi ne na baya-baya da wanda a ke zargin ya aikata, inda ya kashe wata budurwa a wani otel dake a mahadar ababen hawa da ke a garin Fatakwal, inda aka samu gawarta an dora mata wani farin kyalle a wuyanta.