Wata mata ta sace jariri dan wata biyu daga hannun mahaifiyarsa a garin Ado Ekiti babbar birnin jihar. Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a Sakateriyar Ado Ekiti.
Ganau sun bayyana cewa, matar ta yaudari mahaifiyar jaririn, inda ta ce mata ta biyo ta saman Sakateriyar, domin ta amshi wasu kayayyaki da gwamnati ta bayar a matsayin tallafi ga al’umma. “Lokacin da su ka isa sama, sai ta aiki mahaifiyar jaririyar sayan katin waya, inda ta yi awon gaba da jaririn kafin ta dawo,” in ji shaidun gani da ido.
Da ta ke yin bayani a kan lamarin, matar wacce ta ke koka ta bayyana cewa, matar da ta sace mata jariri ta fito ne daga kudancin kasar nan, ta san ta a kasuwar Oja-Oba, kuma ta na sayar da kayayyakin abinci. Ta kara da cewa, a ranar Laraba ce matar ta bayyana mata cewa, za ta kai ta Sakateriya inda mijinta ya ke aiki, domin ta samu kayayyakin da gwamnati ta ke rabawa a matsayin tallafi ga mutane. Matar ta kara da cewa, matar ta zo wurinta a shagonta tare da sunayen wadanda za a ba kayayyakin ciki har da sunanta, inda ta nuna mata cewa ita ce ta taimake ta har a ka saka sunanta a cikin wadanda za a ba tallafin. A cewarta, “matar ita abokiyar kasuwancina ce, inda ta gayyace ni zuwa Sakateriya, bayan mun je, sai ta ce mu jira wani mutum, inda mu ka shiga ofis guda biyu. “Daga baya ta amshi jaririna tare da wayata, inda ta bukaci in siyo mata katin waya, kafin na dawo ta gudu da jaririna,” in ji ta.
Matar ita dai talaka ce, ta bayyana cewa, a kwanan nan ne ta rasa yaronta kafin ta haifi wannan jaririn da a ka sace. Ta ce, matar ta amshi wayarta domin kar ta kira ‘yan sanda lokacin da ta gudu da jaririn.
Sai dai ba a samu kakakin rundunar ‘yan sandar jihar, DSP Caleb Ikechukwu, domin tabbatar da wannan labari ba. Inda wayarsa ta ke kashe lokacin da a ka kira har ya zuwa hada wannan rahoton.