Babban Shehi Malami Sheikh Dahiru Usman Bauchi, yayi kira ga manyan kasa da kungiyoyi da masu fada A ji da su yi kokarin kawo karshen rigimar Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi da Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
Shehin Malamin yayi shelar hakan ne a wata tattaunawa da manema labaru a farfajiyar gidan sa dake Jihar Bauchi.
Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewar,Ya ce duk da dai an samu kurar ta lafa bayan da wasu jagorori suka saka baki, to amma ana bukatar a kuma yima batun zarge musamman daga yankin Arewa don a warware matsalar kwatakwata.
Maganar gaskiya matsalar data faru a tsakanin Masarautar Kano da Gwamnatin Jihar Kano abu ne wanda bai yi dadi ba ko kadan, tun lokacin da matsalar ta fara ruruwa ai sai dana yi magana nace bai kamata irin haka na faruwa a wajen mai muhimmanci kamar jihar Kano ba.
Saboda Jihar Kano cibiya ce da kusan kowa daga bangarori yana amfana da ita musamman Yan Arewa, dalilina kuwa na fadin haka shi ne mafi yawan yan kasuwar mu suna da abokan hulda a Jihar Kano bare kuma a dauki Makaranta Alkur’ani, kai ko me kake yi a Najeriya sai ka sami abokan hulda a Kano; inji shi
Yace masarautar Kano masarauta ce mai tarin daraja da tarihi tun a zamanin baya musamman bangaren al’adu da tarihi.
Yace mu dunga kokarin hakuri don kaucewa rikice rikice.
Jaridar Dimokuradiyya 30-06-019