Wani rahoto da jaridar Daily Nigerian ta labarto, sun bayyana cewa; wani bala’i ya auku a daren ranar Lahadin da ta gabata cikin yankin Mabera dake birnin Shehu wato jihar Sakkwato yayin da wasu dakarun sojin sama suka watsa al’ummar yankin tare da kashe mutane biyu.
Ganau sun bayyana cewa, wannan takaddama ta auku tun yayin da tsokanar wasu matasan yankin ta fuskata budurwar wani babban jami’i na soja. Tsokanar matasan yankin ta sanya takaicin duniya ya ishi wannan budurwa wadda hakan ya sanya ta labartawa saurayinta wanda ya kasance babban jami’in tsaro irin abun da ke ci mata tuwo a kwarya.
Gogan naka bai yi wata-wata ba ya aike da mota guda cike da dakaru domin daukar mataki a kan halin kunci da matasan yankin suka jefa masoyiyarsa. Jaridar Daily Nigerian wadda ta ruwaito rahoton ta ce, sojoji sun bi sahun daya daga cikin matasan wanda ya kasance dalibi, Abdulsalam Lawan, bayan ya tsere har cikin wani gida da ya tare masa hanya.