A jiya Asabar ne Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Sultan na Sakkwato, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya bukaci al’umma musulmi su fara duba jinjirin watan Ramadan na shekarar 1440 A.H. Sarkin Musulim Abubakar ya yi wannna kiran ne ta hannu Farfesa Sambo Junaidu,shugaban kwamitin bada shawara a kan harkokin addini na masarautar sakkwato. Farfesa Junaidu ya kuma kara da cewa, “Ana sanar da Al’umma Musulmi cewa ranar Lahadi 5 ga watan Mayu ne daidai da 29 ga watan Sha’aban 1440A.H., za kuma a fara dyban jinjirin watan Ramadan na shekarar 1440 A.H. “A kan haka ana bukatar Munuslmi sy duba fitowar jinjirin watan Ramadan 1440AH a ranar Lahadi, da zaran kuma an ga watan a sanar hakimi ko sarikin gari mafi kusa don sanar da mai Alfarma kaitsaye.” Sarkin ya kuma yi addu’ar Allah ya taimaki shugabaniun wajen sauke nauyin da Allah ya dora mus na jama’a. Sanarwar ta kuma bayyana cewa, duk wanda ya samu ganin jinjirin watan zai iya tuntubar Fadar Mai Alfarma ta wadannan lambobij wayar kamar haka; 08037157100, 07067416900, 08066303077, 08065480405, 08035965322, 08036149757 da kuma 08035945903.