Mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar (APC), Kashim Shettima, ya ki yin shiru, ya ja kunnen game da cece-kucen da ake tafkawa dangane da tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar kan musulmi da musulmi gabanin babban zabe mai zuwa.
A kwanakin baya ne dan takarar jam’iyyar kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, ya bayyana Shettima a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC.
Ya kare fitowar sa ne a matsayin dan takarar neman mukami na biyu a ranar Juma’a a lokacin da yake jawabi ga mambobin jam’iyyar APC Professional Forum da suka kai masa ziyara a Abuja.
“Suna zarginsa (Tinubu) da yunkurin musuluntar da kasar nan; ya fara musuluntar iyalansa ne?”. dan majalisar ya tambaya.
Shettima, wanda ya taba zama gwamnan jihar Borno har karo biyu, musulmi ne daga yankin arewa maso gabas, kuma dan majalisa mai wakiltar Borno ta tsakiya a majalisar dokokin tarayya da ke Abuja.
Sai dai zabin abokin takarar Tinubu bai yi wa da dama dadi ba, musamman mabiya addinin Kirista a kasar da kuma wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC, ciki har da daya daga cikin abokan takarar shugaban kasa, Mista Babachir Lawal.
Bayan da aka shafe kwanaki ana cece-kuce a kan fitowar sa a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar APC tare da ikirarin cewa jam’iyya mai mulki ta kammala shirye-shiryen musuluntar da kasar nan, Shettima ya yi imanin ‘yan Najeriya ba su da wani abin tsoro.
Sabanin irin wadannan zarge-zarge, ya yi imanin cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ya nuna cewa zai iya tafiya da kowane addini.
Sai dai Shettima, ya roki ‘yan Najeriya da su duba fiye da tunanin addini, su mai da hankali kan yadda za a ciyar da kasar gaba.
“Asiwaju Bola Ahmed Tinubu; eh, abokin takararsa zai iya zama Musulmi, amma abokin rayuwarsa fiye da shekaru 40 ba Kirista ba ne kawai, Fasto ne a Cocin Redeemed Christian Church of God,” in ji shi da yake kare matakin dan takarar shugaban kasa na APC.
“Bai tilastawa addininsa na Musulunci akan ‘ya’yansa ba. Shi ne gwamna na farko da ya mika makarantun mishan ga masu shi, kuma ya zaburar da jama’a daga kowane bangare na rayuwa.
“Ina ganin dole ne mu kalli babban hoto; Aikin da ke gabanmu shi ne mu mayar da wannan al’umma ta zama al’umma mai adalci da gaskiya wadda kowa zai san nasa. Mu ne rabe-rabe na launuka; mu koyi zama da rungumar juna”.