By Abbas Yakubu Yaura
Yanzu haka dai kasar Habasha ta shiga tsaka mai wuya tare da dakaru biyu, wato ‘yan kabilar Tigray (TPLF) da kuma ‘yan kabilar Oromo (OLA) dake yaki da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Abiy Ahmed.
William Davison, wani babban manazarci a kungiyar ICG yace “Yakin ya kara kamari musamman ma daga yankin na Tigray kuma yanzu ya zama abin damuwa na kasa. Hakan ya biyo bayan dokar ta-baci da gwamnatin tarayya ta kafa.”
“Ina ganin babban abin daya kamata a fahimta a yanzu shi ne, a zahiri, yakin yana wajen yankin Tigray ne da farko.Tun daga watan Yuli ne sojojin Tigray suka fara kai hare-hare a yankin Amhara, kuma hakika suna samun gagarumar nasara.Don haka wannan dokar ta-bacin da aka kafa, dokar ta baci ce ta kasa, kuma hakika tana mayar da martani ne tun watan Yuli wadannan runduna biyu suka fara kai farmaki, kuma a yanzu suna cikin wani hali na yi wa gwamnatin tarayya barazana sosai.” a cewar Davidson yace.
A halin da ake ciki, Firaministan Habasha ya bayyana karara cewa ba ya ja da baya. Don haka ya yi kira ga farar hula da su hada kai da sojoji domin kare gidajensu daga sojojin Tigrai dana Romo.
“Abin da muka gani ya zuwa yanzu shi ne raguwar mukamai da kuma daukar matakan da suka dace na firaminista Abiy da abokansa wajen kokarin dakile wannan ci gaban da sojojin na Tigray ke samu,” in ji Davison.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Kungiyar ta TPLF data shafe shekara guda tana yakar gwamnatin Firaminista Abiy Ahmed, ta yi ikirarin samun gagarumar galaba a cikin ‘yan kwanakin nan, tare da kawayenta na Kungiyar ‘Yancin Oromo.
“Haka kuma suna kawance da wata kungiyar ‘yan tawaye ta kabilar Oromo, wannan lamari ne mai matukar hadari. Don haka abin da kasashen duniya ke yi shi ne abin daya dace, wanda ke kira ga dukkan abokan hulda dasu dauki matakin kokarin mayar da wannan lamari zuwa wani salon tattaunawa. Amma a hakika, a wannan mataki, hakan na nufin samun sassaucin ra’ayi da gwamnatin tarayya ta samu, dangane da wannan ci gaban da sojojin na Tigray suke yi. Ya zuwa yanzu, shugabannin tarayya ba su yi wani rangwame ko kadan ba, “in ji Davison.