Shugaban kasa, Bola Tinubu ya taya Mai Martaba Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar III, da Majalisar Sarkin Musulmin Sokoto murnar cika shekaru 67 da haihuwa a ranar 24 ga watan Agusta, 2023, Vanguard ta rawaito.
Shugaban a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce;
“A lokacin farin ciki da godiya ga shugaban darikar Sufaye na Kadiriyya, wanda kuma ke rike da mukamin shugaban kungiyar Jama’atu Nasril Islam kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya.
KARANTA WANNAN: Ambaliyar Ruwa: NEMA ta Raba Kayan Agaji Ga Sama Da Mutane 9k da Abin Ya Shafa
A cewar sanarwar, “Shugaba Tinubu ya amince da sadaukarwar da Sarkin Musulmi ya yi, wanda tun bayan hawansa mulki a watan Nuwambar shekarar 2006, ya yi aiki tukuru don ganin an samu zaman lafiya a kasar nan, kuma bayan haka, ya yi balaguro da kansa, shiga tsakani, da gudanar da tarurruka akan bukatuwar jituwa tsakani al’umma.
“Shugaban ya yaba da martabar Sultan, abokantaka, da makwabcinsa a rayuwa, yana amfani da duk wata dama da suka samu wajen wayar da kan ‘yan kasa kan amfanin son zuciya a cikin al’umma, tare da samar da hanyoyin tabbatar da hadin kan Nijeriya, kamar kafa yarjejeniyar zaman lafiya don zabe a matsayin memba a kwamitin zaman lafiya na kasa.
“Yayin da mai girma tsohon hafsan sojan nan, wanda ya yi wa kasa hidima bisa gagarumin cika shekaru 67, shugaban kasar ya yi imanin cewa kwarewarsa za ta ci gaba da zama wata kadara ga ci gaban al’umma tare da bayar da muhimmanci ta musamman wajen dinke rarrabuwar kawuna na addini, kabilanci da kuma al’adu. ”
Shugaba Tinubu ya yi addu’ar Allah ya kara wa Mai Martaba Sarkin Musulmi lafiya gami da Nisan kwana mai amfani da kuma basira.
A wani labarin kuma, Majalisar Dokokin Kwara ta Tabbatar da Sunayen Kwamishinonin da Gwamna Ya Aike Mata
Majalisar dokokin jihar Kwara, a ranar Talata, ta bayyana tabbatar da jerin sunayen ministocin da gwamna Abdulrahman Abdulrazaq ya mika mata kwanan nan.
Wannan dai na zuwa ne bayan tantance mutane 18 da aka nada a matsayin kwamishinoni da kuma kwamishina guda daya da sunaye biyu na hukumar ma’aikata ta jihar Kwara.