Aku-Uka na masarautar Wukari a jihar Taraba, Dr Shekarau Agyo, ya rasu.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa, Sarkin ya rasu ne a ranar Asabar a fadarsa da ke Wukari bayan doguwar jinya da yi fama da ita.
Marigayi Aku-Uka, mai daraja ta daya kuma shine shugaban majalisar sarakunan jihar Taraba ba ki daya.
An nada shi a matsayin Sarkin na 27 na Wukari a watan Agustan shekarar 1976, kuma an haife shi a shekarar 1937.
KARANTA WANNAN LABARIN: APC ta lashe Dukkannin Kujerun Kananan Hukumomi a Zaben Filato
Wasu majiyoyi na kusa da gwamnatin jihar Taraba, sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa, gwamnan jihar ne kawai zai sanar da rasuwar Aku_Uka a hukumance bayan an gudanar da wasu ayyukan ibada kamar yadda al’adun Yan kabilar Jukun suka tanada.
A wani labarin Kuma na daban.
Mista Mohammed Idris, Shugaban Majalisar Karamar Hukumar Nassarawa Eggon ta Jihar Nasarawa, ya bayyana kaduwarsa kan harin da aka kai wa Waziri Umbugadu Enwongulu, mai ba da shawara kan sha’anin APC na mazabar Wakama.
Yace harin tare da kona gidan na Mista Paul Angbazo, babban dan uwana kuma jigon na APC, bai dace ba kuma basa da tsoron Allah.
Idris ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da yake yin ta’aziyya tare da wanda aka kashe a Wakama, Karamar Hukumar Nassarawa Eggon.Shugaban karamar hukumar, wanda mataimakinsa, Mista Ben Manga ya wakilta, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da dabbanci.
“Ban san dalilin da yasa wasu mutane ba sa son zaman lafiya ba, Me za su samu yanzu da suka rushe wannan gida. “Muna kira ga mazauna Wakama dasu kwantar da hankulansu, su kasance masu bin doka domin jami’an tsaro za su zakulo wadanda suka aikata laifin.
Shi ma da yake jawabi, Messrs Thomas Bawa, Shugaban masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC,da unguwar Wakama, Litinin Nanza, Garba Adigizi da Akolo David, da sauran manyan jiga -jigan jam’iyyar, sun yi Allah wadai da harin baki daya.
Sun bukaci hukumomin tsaro dasu kamo wadanda suka aikata munanan ayyukan tare da tabbatar da hukunta su daidai da dokokin da suka dace.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa a ranar 7 ga watan Oktoba, Hukumar zabe mai zaman kanta ta Jihar Nasarawa ta bayyana cewa jam’iyar APC ta lashe dukkan shugabanci kujeru 13 da mukaman kansiloli 147 a zaben kananan hukumomi da aka gudanar a ranar 6 ga watan Oktoba.
Comments 2