A yau ne garin Gashua shedikwatar karamar hukumar Bade a jihar Yobe ya tashi da tashin hankalin da wasu matasa da suka fusata suka yi kan harbin wani direba a wani gidan mai da yammacin jiya.
A halin yanzu ’yan bangar sun tare titin Filin Tanda tare da kona tayoyi a yayin da suke rera wasu taken neman a binciki lamarin.
Wani mazaunin unguwar wanda ya shaidawa gidan talabijin na Tvc News cewa a yammacin jiya ne wasu mutane da aka gani sanye da kakin sojoji suka zo wani gidan mai a kan babura kawunansu a rufe, suka bukaci kowa ya nutsu, wani direban da ya tsorata ya yi yunkurin tserewa aka harbe shi, wannan ne ya jawo zanga-zangar”.
Hukumar ‘yan sanda da gwamnati har yanzu ba su ce uffan ba kan wannan mummunan lamari.