Yadda wani Ɗan Ta’adda mai mabiya 3000 ke bayyana kuɗin fansa daya karba a Tiktok
An ba da rahoton cewa an ga wani dan ta’adda a wani faifan bidiyo da ke nuna wasu kudade da aka karba daga hannun wadanda abin ya shafa a matsayin kudin fansa a shafin Tiktok.
Zagazola Makama, kwararre ne kan yaki da tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a tafkin Chadi, ne ya raba bidiyon a cikin jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na X ranar Litinin.
KARANTA WANNAN LABARIN:Kotu ta kori karar da ke neman dakatar da gudanar da zabe, jarrabawa a ranar Asabar
A cewar Makama, wanda ke amfani da shafin yana da mabiya sama da 3000, inda ya ce wasu daga cikinsu ‘yan bindiga ne da ke fito da bindigoginsu a fili kuma suna sanye da kayan soja ko na ‘yan sanda.
Ya kuma koka da yadda dandalin Tiktok ya baiwa masu tada kayar baya damar tallata yakinsu na ta’addanci ba tare da wani takunkumi ba.
Ya rubuta: “ ‘Yan ta’adda a Tiktok suna faduwa da nuna kudin fansa da suka karba daga wadanda abin ya shafa.
“Mai amfani da shafin yana da mabiya 3000, wasu daga cikinsu ‘yan fashi ne da ke fito da bindigoginsu a fili kuma suna sanye da kayan sojoji ko na ‘yan sanda.
“Tsarin Tiktok ya bai wa ‘yan tada damar tallata yakin ta’addanci ba tare da an takura su ba.
A wani labarin kuma:Kotu ta hana Murja Kunya amfani da kafafen sada zumunta
Wata babbar kotun jihar Kano karkashin jagorancin mai shari’a Nasiru Saminu a ranar Litinin ta bayar da belin Murja Kunya a kan kudi naira 500,000.
Ƴar TikTok ɗin dai ta nemi a bayar da belinta ne, biyo bayan umarnin da kotun shari’ar Musulunci ta Kano ta bayar na cewa wani likitan tabin hankali ya duba lafiyarta.