Akalla mutane 11 ne aka kashe bayan wasu ‘yan bindiga dauke da manyan muggan makamai sun kai hari a wasu kauyukan karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina.
Wadanda suka shaida lamarin sun shaida wa manema labarai cewa da isar su a daren ranar Talata, ‘yan bindigar sun yi ta harbe-harbe ta iska kafin su tafi gida gida domin neman wadanda suka lamarin ya rutsa da su.
Rahotanni sun Kuma nuna cewa, ‘yan bindigar sun kai farmaki ne a kauyukan da bai gaza biyar ba a cikin karamar hukumar.
Mazauna yankin sun ce, a yayin farmakin da aka kai cikin dare, an kuma jikkata mutane 13 tare da kona gidaje da dama, yayin da ‘yan bindigar suka fara Kai farmakin tun daga magariba har zuwa wayewar garin yau Laraba.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan bindiga sun kashe Matan Aure da wasu Mutane 12 a Taraba
Da yake tabbatar da faruwar lamarin a yau, hukumomin rundunar ‘yan sanda a jihar sun bayyana cewa, yankunan da da aka kai wa harin sun hada da, Katoge da Yanturaku.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Gambo Isah, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce ‘yan bindigar sun zo ne da bindigar AK 47 ba da gangan ba.
Ya kuma kara da cewa rundunar ta tura mataimakin kwamishinan ayyuka tare da karin wasu rukunin ‘yan sanda domin Tsaurara Mayakan tsaro a yankin.
Kazalika ya Kuma bayyana cewa, An binne wadanda aka kashe a harin na daren jiya a garin Batsari kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
A wani labarin Kuma na makamancin wannan
Darakta, ilimi da ci gaban zamantakewa na karamar hukumar Zariya, Misis Deborah Mugu; tace Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mataimakinta, Dalhatu Aliyu-Awai tare da wasu ma’aikata 11 a garin Kidandan da ke karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna a ranar Litinin.
Wata majiyar tsaro ta shaida wa jaridar Daily Trust cewa wadanda abin ya shafa na dawowa ne daga ziyarar jaje da wani ma’aikacin Karamar hukumar ya rasa mahaifinsa a lokacin da ‘yan bindiga suka tare su, da misalin karfe 1:30 na rana.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun sako Umar Abubakar (Katako) direban motar bas mai dauke da mutane 18, inda suka bukaci ya koma gida ya sanar da ‘yan uwa cewa, an yi awon gaba da wasu ma’aikatan.
Ya ce bisa ga rahoton da ya faru a kan idonsa, ‘yan bindiga 6 dauke da AK47 sun dira motar bas din mintuna 45 bayan ta taso daga garin Kaya. Ya ce bayan sun yi bincike tare da kwashe fasinjojin da kayayyakin masu daraja, inda ‘yan bindigan sun kai su wani yanki na daji.
Ya lissafa sauran wadanda abin ya shafa kamar haka: Sulaiman Zailani, Nura Abdullahi, Umar Shehu, Halima Tabari, Fatima Abdullahi da Hafsat Zakari.
Sauran sun hada da Maryam D, Hulaila Fate, Hajara Muhammad, Kuluwa Isa da Amina Sulaiman.
Comments 1