Rundunar sojin Kasar Burkina Faso ta ce ta rasa akalla dakarunta 7 yayin da ta hallaka Yan ta’adda 20 biyo bayan wani bata-kashi a sansanin soji biyu dake Arewacin kasar.
Kana hudu daga cikin dakarun Sakai dake taimakawa rundunar sun mutu yayin Wani hari a gundumar Loroum da Sanmatenga kamar yadda sanarwar rundunar ta bayyana.
Rundunar sojin ta kuma yi ikirarin kwacewa tare da lallata makamai, Motoci da kayayyakin sadarwa na maharan.
Hare-haren na zuwa ne kwana guda bayan kashe wani jami’in soji guda da jikkata wani, yayin da wata nakiya ta Tashi a Arewacin Kasar.
A wani labarin Kuma na daban.
Yayin da ake ci gaba da tsare jagoran ‘yan asalin yankin Biafra, Nnamdi Kanu da kuma yunƙurin neman shugabancin ƙasar Igbo a 2023, shugaba Muhammadu Buhari ya gana da Ohanaeze Ndígbo da shugabannin yankin kudu maso gabas a jihar Ebonyi.
Wakilan Kudu-maso-Gabas da suka gana da Buhari a ranar Juma’a a sabon dakin taro na exco Chambers,a gidan gwamnati dake Abakaliki sun samu jagorancin shugaban kungiyar Ohanaeze, George Obiozor,
Ko da yake ba a iya samun cikakken bayanin taron ba, Ohanaeze a wata sanarwa daya fitar ranar Talata a karshen taronta da aka gudanar a Abakaliki, ta ce ziyarar aiki ta kwanaki biyu da Buhari zai kai Ebonyi, za ta fara aiwatar da shirin ne domin a samu saukin sakin Kanu tare da matsa kaimi wajen ganin an sako Kanu Shugaban ‘yan kabilar Igbo a Najeriya.
Sanarwar ta kara da cewa, “Ohanaeze Ndigbo Worldwide ta bayar da tabbacin zaman lafiya da tsaro gabanin ziyarar da shugaban kasa zai kai jihar Ebonyi….Amma fatan Ndigbo shine a yi amfani da irin wannan tagomashin don samun sakamako mai kyau domin shugaba Buhari zai samu nasara da Ndigbo.
Wannan zai kasance daya daga cikin manyan ziyarar da mai girma shugaban kasa zai kai yankin Kudu maso Gabas, domin muna sa ran ziyarar aiki ta kwanaki biyu da shugaban kasa zai yi a jihar Ebonyi za ta sauya labarin cewa Buhari na son Ndigbo, kuma zai tabbatar da hakan ta hanyar kaddamar da yakin neman zabe. tsarin da zai saki Nnamdi Kanu.”
“Ya kamata kungiyar IPOB da sauran masu fafutukar kafa kasar Biafra su ci gaba da zaman lafiya kuma su kasance masu biyayya ga tsarin da zai taimaka musu wajen ganin an sako shugabansu, Mazi Nnamdi Kanu.
Ziyarar ta Buhari za ta haifar da sabon fata na samun shugaban Najeriya na ‘yan kabilar Igbo da kuma tabbatar da sakin Mazi Nnamdi Kanu.”