Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani tsoho dan shekara 54 mai suna Mamman Bayero, sannan kuma sun jikkata wan matashi mai suna Mohammed Ibrahim, a kauyen Kadunu da ke karkashin karamar hukumar Mangu a jihar Filato.
DSP Terna Tyopev, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ya tabbatarwa manema labarai da faruwan hakan a ranar Litinin inda ya ce abin ya faru ne a ranar Lahadi. Tyopev ya ce “jiya da misalin karfe 7:45 na dare mu ka samu rahoto daga ofishin ‘yan sanda dake Mangu a kan cewa wasu ‘yan bindiga suna kashe wani tsoho, Mamman Bayaro, dan shekara 54 daga kauyen Kadunu da ke karkashin karamar hukumar Mangu.”
Ya ci gaba da cewa; “Sakamakon harin, an harbe mamacin a kirji sannan da aka garzaya da shi zuwa asibitin Allah Na Kowa domin yi masa magani a nan ne likitoci aka tabbatar da cewa ya mutu. Haka zalika wani matashi Muhammadu Ibrahim daga wannan kauyen ya jikkata sakamakon haren da ‘yan bindigan suka kai a yayin da suka harbe shi a kafa, a halin yanzu yana asibiti ana kula da lafiyarsa.”
Jami’in hulda da jama’ar ya ce rundunar na iya kokarinta wajen ganin ta kama wadanda suka aikata wannan mummunar hari domin a yi masu hukuncin wanda ya cancanta da su.