‘Yan banga 63 da aka fi sani da ‘Yan Sa Kai, an ba da rahoton cewa ‘yan bindiga sun kashe su.
A cewar BBC, wannan mummunan lamari ya faru ne bayan da jami’an tsaron yankin suka kaddamar da farmaki kan ‘yan bindigar a masarautar Zuru ta jihar Kebbi.
An kashe mutanen da aka yi jana’izar ne da sanyin safiyar ranar Litinin.
An ce ‘yan bindigar sun boye ne a kan bishiyoyin da ke kan hanyar da ke zuwa maboyar su.
An ce sun bude wuta ne bayan da ‘yan bangan suka afka tsakiyar maharan.
Yan-Sa-Kai sun fito ne daga garuruwa da kauyuka daban-daban na masarautar.
Hukumomin jihar ba su mayar da martani kan wannan mummunan lamari ba har ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.