Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da basaraken Owa-Onire a gundumar Kwara ta Kudu dake jihar Kwara.
DAILY POST ta samu labarin cewa an yi garkuwa da shi tare da matarsa da direban sa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Magoya bayan Obi Sun Kalubalanci Yan Sandan Jihar Legas
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Okasanmi Ajayi, ya tabbatar da faruwar lamarin ga jaridar Majiyar Jaridar Dimokuradiyya a ranar Asabar.
Okasanmi ya bayyana cewa yanzu haka mutane biyu da ake zargi suna hannun ‘yan sanda kan lamarin.
Ya kara da cewa an ceto matar sarkin, yayin da ake ci gaba da kokarin ceto sauran biyun da suka rage.
A cewar Okasanmi, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Paul Odama, ya aike da tawagar masu bincike tare da ‘yan banga zuwa wurin.
Kakakin ya ce za a bayyana cikakken rahoto da zarar an kammala bincike kan lamarin.
Wannan dai shi ne karo na farko da aka yi garkuwa da wani a jihar tun bayan da sabon kwamishinan ‘yan sandan ya hau ofishin a watan jiya
A WANI LABARIN KUMA: Alamun Fili Dana Ɓoye Sun Tabbatar Da PDP Zata Kwace Najeriya A 2023 – Atiku
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya ce jam’iyyarsa na da kyakkyawar damar yin nasara a zaben baɗin dake tafe.
“PDP tana da damar lashe zaben shugaban kasa kasancewar ta daya daga cikin tsofaffin jam’iyyun siyasar kasar.”