Wasu ’yan bindiga wadanda ba a san su waye ba sun sace hakimin mahaifar shugaban Najeiya Muhammadu Buhari da ke birnin Daura, Alhaji Musa Umar, a daren jiya. Kamfanin dillancin labarai na Najeriya, NAN, ya ruwaito cewa masu satar mutanen sun tsinkayi gidan ne da misalin karfe 7:00 na daren Larabar jiya, inda su ka rika yin ruwan wuta a iska, su na tsorata mutane, wadanda su ka rika arcewa domin tsira da rayuwarsu. Majiyar ta nuna cewa, lamarin ya faru ne bayan hakimin ya dawo daga sallar Magariba ya zauna a kofar gida tare da wasu daga cikin ’yan fadarsa. Hakimin, wanda a ka ruwaito cewa surukin dogarin shugaban kasa ne, wadanda su kama shi din su iso a cikin mota kirar Fijo 406 ne. Bayanai sun nuna cewa, bayan faruwar lamarin shugaban karamar hukumar Daura, Malam Abba Mato, da daruruwan masu jajentawa sun halarta a gidan hakimin, saboda nuna jimami. Garkuwa da mutane dai ya zama ruwan dare a Arewacin Najeriya, inda ko a ranar Litinin da ta gabata an kama shugaban hukumar ilimi tun daga tushe na kasa (UBEC), Dr. Mohammad Mahmood Abubakar tare da diyarsa, Yasmin Mohammed, sannan a ka kashe direbansa a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja. Amma daga bisani ‘yan sanda sun tserar da su washegari bayan da a ka ce an biya fansa. A taron da a ka gudanar na watanni uku da a ka saba yi da sakarunan gargajiya a Kaduna ranar Talata, mai rikon mukamin Babban Sufeton ’Yan Sanda Na Kasa, Alhaji Mohammed Adamu, ya ce, an yi asarar rayuka 1,071 sakamakon aikata miyagun laifuka a fadin kasar cikin 2019 din nan kacal. Sannan a tsakanin watan Janairu an yi garkuwa da mutane akalla 685 a kasar, inda ya ce mutum 767 kuma an kashe su ne a Arewa. Bugu da kari, Adamu ya yi karin haske da cewa, an fi rasa rayuka a Arewa maso Yamma inda mutum 436 su ka rasu; Arewa ta Tsakiya kuma ke biye da mutum 250; yayin da a Kudu maso Kudu a ka rasa rayuka 130 a tsawon lokacin. Ya kara da cewa, a jihar Zamfara kadai an samu aikata laifukan kisan kai har guda 203, inda nan ne ya fi ko’ina fuskantar matsalar. Sai kuma jihar Kaduna da ke biye da adadin 112, yayin da jihar Biniwe ta biyo su da 90.