Rundunar Yan sanda a Jihar Bauchi za ta hukunta wani jami’in ta da aka kama da musguna wa wani dan jarida mai aiki da gidan talabijin na kasa NTA mai suna Halliru Ahmad.
A ranar Lahadi ne dan jaridar ya koka bisa cin zarafin da ya ce wabi jami’in dan sanda ya yi masa a filin wasa na tunawa da Marigayi Sir Abubakar Tafawa Balewa dake Bauchi yayin da ya je ɗaukar rahotanni.
Wannan matakin hukunta dan sanda ya biyo bayan wata zama sulhu ne da Kwamishiniyar yan sandar Jihar DCP Rose Dachollom ta yi da manyan jami’an kungiyar yan jarida ta kasa dake Bauchi.
Yayin taron an tuhumi dan sandar da wuce gona da iri kuma shi ma da kansa ya amsa laifinsa.
Wata sanarwa da Shugaban Ƙungiyar yan Jarida ta Jihar Bauchi Kwamared Umar Sa’idu ya fitar, ta bayyana yadda rundunar ta nemi gafarar ƙungiyar tare da bayyana cewa makamancin hala ba zai kara faruwa ba.
Idan za’a iya tunawa dai a ranar Lahadin da ta gabata ne al’amarin ya faru sa’ilin da Dan jaridar ke kokarin shiga daukar rahotannin kafzawa tsakanin kungiyar Wikki Tourist da Akwa United a gasar Firimiyar Najeriya.