Kimanin mutum 26 suka gamu da ajalinsu sakamakon wani harin ta’addancin da ake kyautata zaton mayakan jihadi ne suka kai shi a wani kauyen da ke tsakiyar kasar Mali.
Shedun gani da ido sun tabbatar wa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP da cewa harin ta’addancin ya auku ne a wani garin da galibinsa na ‘yan kabilar Fulani mai suna Binedema a yankin Mopti da ke tsakiyar kasar.
Tun a shekarar 2015 ne dai yankin na tsakiyar kasar Mali ke fama da matsalolin hare-haren sari ka noki da na ramuwar gayya tsakankanin manyan kabilun yankin, baya ga wasu dimbin hare-haren ta’addancin da masu mubaya’a ga shehin Malamin nan Amadou Koufa da ya sallama wuya ga kungiyoyin da’awar jihadin kasar ke kaiwa.