Makonni kadan bayan harin da aka kaiwa ayarin motocin shugaban kasa Muhammadu Buhari a jihar Katsina, ‘yan ta’adda sun yi barazanar sace shugaban kasar.
An kaiwa ayarin tawagar shugaban kasa hari akan hanyarsu ta zuwa mahaifar Buhari dake Daura gabanin Sallah.
A yayin harin, Mutane biyu sun samu raunuka, wanda fadar shugaban kasar ta ce an dakile.
Harin da aka kai wa ayarin motocin ya faru ne a ranar da ‘yan ta’addar a yankin yammacin Afirka (ISWAP) suka mamaye gidan yarin Kuje da ke Abuja tare da kubutar da fursunoni sama da 800 da suka hada da daukacin ‘yan ta’addan da ake tsare da su.
JARIDAR DIMOKURAƊIYYA ta rawaito yadda masu garkuwa da jirgin suka yi murna lokacin da aka sako fursunonin Kuje.
A wani sabon faifan bidiyo da suka saki, ‘yan ta’addan da suka yi garkuwa da fasinjoji sama da 60 a cikin jirgin kasa na Abuja Kaduna a ranar 28 ga watan Maris, sun yi barazanar sace Buhari da Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai tare da kashe su.
‘Yan ta’addan sun kuma yi alfahari da cewa za su ruguza kasar, su kashe sauran fasinjojin da ke hannunsu sannan su sayar da sauran.
An sako wasu fasinjojin ne bayan da aka ce sun biya kowannen su Naira miliyan 100.