Dan takarar jam’iyyar PDP a majalissar wakilai na mazabar Irewole/Isokan/Ayedaade, a jihar Osun a zaben 2023, Mista Sola Arabambi, ya rasu.
Wani mataimaki ga marigayi Arabambi, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce shugaban nasa ya rasu ne a ranar Asabar a wata gajeriyar rashin lafiya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sanata Uba Sani Ya Bada Tallafin Karatu Ga Wasu Dalibai A Jihar Kaduna
A cikin wata sanarwa da ofishin yada labaran sa ya fitar, tsohon dan takarar kujerar gwamna a jam’iyyar PDP a jihar Osun, Prince Dotun Babayemi, ya ce mutuwar Arabambi ta yi zafi, inda ya bayyana shi a matsayin mutum mai gaskiya game da burinsa na yi wa al’ummarsa hidima.
Sanarwar ta kara da cewa, “Hakika, labarin rasuwar Sola ya zo min a cikin rashin jindadi. Mutum ne mai hidima. Ya taba rayuka da dama da yake iya kaiwa, don haka ba za a manta da gudunmawar da ya bayar ba.”
Da yake jajantawa ‘yan uwa da jam’iyyar da kuma al’ummar mazabar tarayya bisa rasuwar, Babayemi ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayin, ya kuma baiwa iyalansa hakurin jure rashinsa.
A wani labarin kuma, 2023: Zan Rage Rashin Aiki Da Kashi 50 A Shekara Ta Farko — Kola Abiola
Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PRP, Kola Abiola ya ce idan aka zabe shi a zaben 2023, zai rage rabin yawan marasa aikin yi a kasar nan.
Alkaluman baya-bayan nan da Hukumar kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar ya nuna cewa rashin aikin yi a Najeriya ya kai kashi 33.3 bisa dari a rubu’i na hudu na shekarar 2020.
Abiola, wanda ya yi magana a ranar Juma’a a yayin wani shiri kai tsaye a gidan Talabijin na Channels Politics Today, ya ce zai ba da fifiko mai dorewa da rarrabawa don bunkasa tattalin arzikin kasar.