Wata Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Filin Hoki a Kano, ta tasa keyar wata fitacciyar ‘yar TikTok Murja Ibrahim Kunya a gidan gyaran hali bisa zargin ta da aikata laifukan da suka saba wa koyarwar addinin Musulunci da kuma yi wa mutane barazana a Tiktok.
Murja ta bayyana a gaban kotun da Abdullahi Halliru ke jagoranta bisa wasu tuhume-tuhume guda biyu da suka hada da barazanar kai hari ga wasu mutane da kuma fitar da bidiyoyi masu tayar da hankali da suka saba wa ka’ida da koyarwar addinin Musulunci, wanda hakan na iya jawo wasu kuskure.
KARANTA WANNAN LABARIN: Tafiye-Tafiyen Da Buhari Ya Yi Zuwa Kasashen Waje Bai Wadatar Ba – Onyeama
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa ‘yan sanda sun kama Murja Ibrahim Kunya ‘yar TikTok ne sakamakon korafin da Majalisar Malamai ta gabatar.
Sai dai a lokacin da aka gurfanar da ita a gaban kotu, ta musanta zargin da ake mata.
Alkalin ya dage sauraron karar zuwa ranar 16 ga watan Fabrairu, 2023, don ci gaba da sauraren karar, sannan ya bayar da umarnin a tsare wanda ake tuhuma a gidan gyaran hali.
A halin da ake ciki, lauya ga Murja Kunya, Barista Yasir Musa, ya roki kotun da ta tura ta hannun Hisbah ko kuma ‘yan sanda a maimakon gidan gyaran hali, wanda majalisar ta ki amincewa da wadanda ake kara da Barista Lamido ABBA Soron Dinki ya yi.
A wani labarin kuma, U-20 AFCON: Young Chipolopolo Ta Zambia Sun Isa Abuja Domin Buga Wasan Sada Zumunci Da Flying Eagles
Tawagar ‘yan kasa da shekara 20 ta Zambia, Young Chipolopolo, ta isa Abuja da yammacin ranar Alhamis domin buga wasan sada zumunci da kungiyar Flying Eagles.
‘Yan wasa 23 da suka hada da kwararrun ma’aikata da manyan jami’an hukumar kwallon kafar Zambia sun isa filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da misalin karfe 3 na rana.