JARIDAR DIMOKURADIYYA: Yau Laraba 10-04-2019 ta zo dai da ranar da aka haifi Attajiri Aliko Dangote.
Rahotanni sun bayyana cewar an haifi Alhaji Aliko Dangote a jihar Kanon Dabo, a daidai ranar goma ga watan Afurelun shekarar 1957.
Attajiri Aliko da Danginsa sun gaji dunbin dukiya wanda hakan ya bashi damar fara kasuwanci tun yana matashi mai kananan shekarun kuruciya.
A bangaren ilimi Attajiri Aliko yayi karatun addini, Allo dana zamani, kafin daga bisani ya koma Kurmi da zama don gudanar da harkokin kasuwanci…..
Masana sun sha karo kan cewa har yanzu Aliko Dangote bai san adadin dukiyar sa ba.
A wata hira da aka yi da shi a makon daya gabata Aliko yace baya yawo da ko Sisin kwabo a cikin Aljihun sa, hasalima sau daya ya taba rubuta chaki ta ciro kudi Dala miliyan Goma don ya gazgata cewar yana da dukiya.
Muna Adduar Allah ya ci gaba da sanyawa rayuwarka Albarka.