Hukumar ƙwallon ƙafa ta kudancin nahiyar Amurka ta bayyana cewa za’a fara fafata wasannin neman cancantar buga gasar cin kofin duniya a nahiyar a wata mai kamawa na Oktoba wato watan goma kenan.
A sabo da haka nema dole ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa su bar ‘yan wasa suzo su wakilci ƙasar su duba da cewar kishin ƙasar ne a zuciyar ‘yan wasan tunda ƙasarce tushen ɗaukakar su lokacin da suka fara fafata wasan ƙwallon ƙafa.
Tuni hukumar ta fitar da jerin wasannin da daza a fafata wanda daman su kudancin Amurka nasu wasannin neman cancantar ya bambanta daba kowacce nahiya inda su nasu babu batun raba rukuni, sai kowacce ƙasa ta fafata da kowacce.
Tuni dai ita kanta ƙasar Argentina wadda tayi shuhura a dunuyar ta ƙwallon ƙafa zata fara fafata wasan farko da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Ecuardo a birnin La Bombonera sannan kwanaki kaɗan kuma ta sake fafata wasa karo na da ƙasar Bolivia a birnin La Paz.
Ana ganin wannan shine gasar cin kofin duniya na ƙarshe da Messi zai fafata matuƙar ƙasar Argentina ta sami tikiti wanda ƙasar Qatar zata karɓi baƙunci nan da shekaru biyu masu zuwa wanda idan dai har Argentina basu lashe gasar ba to Messi zai kammala wasansa ba tare da ya lashe gasar cin kofin duniya ba.
Idan za a iya tunawa Argentina ta kai ga matakin wasan ƙarshe na gasar ta cin kofin duniya a shekarar 2014 da ƙasar Brazil ta karɓi baƙunci inda ƙasar Jamus ta lashe ta daci 1 mai ban haushi.