Gwamnonin yankin kudu masu kasar nan a jiya talata, sun yi wata ganewa a jihar Legas domin lamura da suka shafi tsaro da kuma dangogin su a yankin.
Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Ondo Rotimi Akeredolu ne ya jagoranta taron wanda ya gudanar a fadar Legas dake garin Marina a jihar.
A dai karshen taron wanda aka shafe tsawon lokaci a na ayyuka, Gwamna Akeredolu yace, daga cikin dalilan da suka shafi dan gane da matsalar tsaro a yankin, sun hada da damuwa da za abi domin matsalar.
Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da mai masaukin baki Gwamna Babajide Sanwo-Olu, da gwamnan Osun Gboyega Oyetola, da Dapo Abiodun na jihar Ogun, da kuma Kayode Fayemi na jihar Ekiti.
KARANTA WANNAN LABARIN: Hukumar NCDC ta fitar da Sabbin Alkaliman wadanda suka kamu da Corona a Nigeria
Sai dai duk da cewa, gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo bai halarci taron ba, amma ya sami damar nunasa Rauf Olaniyan.
Kazalika bayan taron tattaunawan sun kuma ziyarci jigon jam’iyar APC na kasa Bola Tinubu, wanda bai jima da dawuwa daga kasar ba domin duba lafiyar sa.