Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi, ya yi alkawarin cewa zai gyara titin Shintakun-Oguma-Gboloko-Mozum dake karamar hukumar Bassa idan har aka sake zabarsa a zaben gwamna da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamban nan.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a Fadar Sarkin Aguma na Bassa, Cif Williams Keke, a yayin da ya kai masa ziyara domin samun albarkar Sarkin bisa neman sake zabarsa a karo na biyu a matsayin gwamnan jihar Kogi, a wani mataki na kamfen da ya je yankin.
Bello ya yi alkawarin bai wa gyaran tituna a fadin jihar muhimmanci a wa’adin mulkinsa na biyu idan har ya lashe zaben da za a yi. Inda ya ce gyaran titunan zai taimaka matuka gaya wajen zirga-zirga da ababen hawa, kuma hakan a cewarsa zai taimakawa manoma wajen fitar da abubuwan da suke nomawa a karkara zuwa kasuwannin dake Birane.
A na sa jawabin, Sarkin ya jinjinawa gwamnan bisa irin namijin kokarin gwamnatin Yahaya Bello wajen bunkasa walwalar al’ummar jihar Kogi.