An hallaka wani dan bijilanti mai suna Auwal Muhammad yayin wani bata-kashi da masu garkuwa da mutane a kauyen Agbudu dake karamar hukumar Koton-Karfe ta jihar Kogi.
Wani dan bijilantin da ya bukaci a sakaye sunan shi, shine ya tabbatar da aukuwar wannan lamari inda ya ce kuma ya faru ne a daren jiya talata.
Ya kara da cewa wannan bata-kashi ya biyo bayan wani yunkurin da yayan kungiyar ne suka yi na wargaza sansanin masu garkuwa da mutanen a wani gandun daji dake kusa da kauyen na Agbudu.
Kuma tuni aka yi jana’izar Mamacin kamar yadda addinin Islama ya koyar.
Kawo yanzu dai Kakakin rundunar yan sandar Jihar bai ce uffan ba dangane da wannan lamari.