• MDD ta sake zaban Amina Mohammed domin cigaba da rike matsayin ta.
•Antonio Guterres ne ya bukaci da ta cigaba da rike mukamin nata a karo na biyu.
•Amina ta amince ta cigaba da kasancewa mataimakiyar sakataran MDD.
An sake zabar yar Najeriya Amina Mohammed, a matsayin mataimakiyar sakataran majalissar dinkin duniya.
A jiya juma’a ce dai, Antonio Guterres ya sake ba ta rikun wannan mukami a zango na biyu, jim kadan bayan kammala taron majalissar, da ta bai wa Antonio daman rike matsayin shi a karo na biyu.
Zangon Guterres na biyu, zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2022 me zuwa, kuma zai rike mukamin ne, na tsawon shekaru biyar masu zuwa.
Idan za a iya tunawa dai, Guterres ya gaji Mr Ban Ki-moon ne, a matsayin sakataran MDD, tun a watan Janairun shekarar 2017.
KARANTA WANNAN: wani dan kwallo Nijeriya ya auri yar film
Bugu da kari, a lokacin da yake jawabi ga manema labarai, jim kadan bayan ya sha rantsuwar kama aiki, Guterres ya tsawaita wa Amina Mohammed aikin ta.
Ya ce, “bayan an sake zaba na, don haka ina farin cikin bai wa mataimakiya na, damar cigaba da aiki da ni a zango na biyu, wanda kuma na ke fatan za ta amince da shi,” inji Guterres.
Ana ta bangaren Amina Mohammed, wacce ta ke tsaye kusa da Guterres lokacin zantawar, ta ce, “na amshi wannan tayin,” inji ta.
Amina dai, yar difulomasiyya ce, kuma yar siyasa, wacce ita ce ta biyar, da ta ke rike, da mukamin na mataimakiyar sakataran MDD.
Comments 1